Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA -bayyana cewa an fara tashe-tashen hankula na baya-bayan nan ne, a lokacinda wani dan majalisar dokokin gwamnatin Yahudawa mai suna Itamar Ben Gvir ya bude majalisa a unguwar Shiekh Jarrah da nufin tattabatar da cewa an kori dukkan Falasdinawan da suke da gidajensu a unguwan don yahudawa su shiga gidajensu.
Tawagar kungiyar tarayyar Turai zuwa ga gwamnatin Falasdinawa ta bukaci a kawo karshen tashe-tashen hankulan ne a shafinta na Twitter. Tawagar ta zargi yahudawa masu tsatsauran ra’ayi da tada rikici na baya-bayan nan a unguwar.
A bangaren Falasdinawa kuma gwamnatin Shugaban Mahmood Abbas ta dora dukkan laifin abubuwan da suke faruwa a unguwar Shiekh Jarrah kan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila, wacce take son sauya yanayin birnin Qudus gaba daya.
342/